Duniya

Sabon Jagoran Addinin Iran Ya Tsira Daga Yunkurin Kai Masa Hare-Hare Guda Biyu

Wani dan majalisar dokokin Iran ya bayyana cewa sabon jagoran addinin kasar, Mojtaba Khamenei, ya tsira daga hare-hare biyu da aka kai masa.

A cewar rahoton kamfanin dillancin labaran gwamnatin Iran, dan majalisar da ke wakiltar Jahrom, Mohammad Reza Rezaei Kochi, ya ce Mojtaba Khamenei yana tare da mahaifinsa, Ali Khamenei, lokacin da aka kai hari kan gidan jagoran addinin, amma ya tsira daga yunkurin kashe shi.

Kochi ya kuma bayyana cewa an sake kai wani hari a wani asibiti a lokacin da sabon jagoran ke wurin, amma ya ce United States da Israel ba su cimma burinsu ba.

Sai dai dan majalisar bai bayyana sunan asibitin ko wurin da aka kai harin ba.

Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce a wata hira da tashar Fox News cewa sabon jagoran Iran ya samu rauni a ranar farko ta hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai. Ya kara da cewa yana kyautata zaton jagoran yana raye, sai dai an ji masa rauni.

A ranar Laraba kuma aka wallafa sakon farko daga Mojtaba Khamenei, inda ya bayyana cewa Iran za ta dauki fansar mutanenta da aka kashe a hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai wa kasar.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker