Labarai

Gwamnatin jihar Bauchi ta dakatar da sarkin Misau

Gwamna Bala Muhammad ya amince da dakatar da Me Martaba Sarkin Misau Alhaji Ahmad Suleiman.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin kaddamar da kwamitin bincike kan rikicin da ya afku a Zadawa dake karamar hukumar Misau da yayi sanadiyar rasa rayuka.

Yayin kaddamar da kwamitin a gidan gwamnati, Gwamna Bala Muhammad yace matakin dakatar da Sarkin, shugaban karamar hukumar da kuma wasu shugabannin yankin ya zama wajibi don bada kwamitin damar bincike da kuma zama izina ga masu zagon kasa ga zaman lafiya a jihar Bauchi.

Yayin taron, Gwamna Bala Muhammad ya rantsar da sabon shugaban rikon karamar hukumar Honorable Isah Kufai tare da kiransa da yayi aiki da kwamitin da aka kafa don lalubo musabbabin rikicin.

A cewar Lawal Muazu Bauchi me tallafawa Gwamna Bala Muhammad kan kafafen yada labarai na zamani.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

  • YAHAYA SHUAIBU

    Popularly known as Yahmis Yahaya a Media Technology Professional and Journalist with extensive experience in digital media, broadcasting technology, streaming services, and online publishing. He specializes in leveraging technology to enhance news production, content distribution, and audience engagement. As the Founder of Hausa360 Media and a media technology practitioner, he is passionate about digital journalism, technology reporting, media innovation, and the use of emerging technologies to strengthen information access and public communication.

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker