Kiwon Lafiya

Gwamnatin Filato ta samar da maganin maciji kyauta ga al’umma

Gwamnatin Jihar Filato karkashin jagorancin Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang ta samu gagarumar nasara ta hanyar shirin bayar da maganin maciji kyauta. An yi nasarar warkar da mutane 311 daga cikin 312 da macizai suka ciza tsakanin watan Disamba 2025 da Yuni 2026.

Bayan amfani, karbar da rarraba maganin Echitab® Anti-Snake Venom zuwa cibiyoyin lafiya a kananan hukumomi 15, mazauna yankin sun sami saukin samun magani ba tare da matsalar kudi ba.

Wannan shiri ya kara wa jama’a karfin gwiwa wajen neman magani, ya rage mace-macen da akeyi sanadin cizon maciji, kuma ya inganta ayyukan gaggawa a fadin jihar plato.

Yayin da lokacin noma ke gabatowa, lokacin da ake yawan samun cizon macizai, Gwamna Mutfwang ya sake amincewa da siyan karin maganin maciji don rarraba wa a fadin jihar.

Karin Sayan maganin na nufin tabbatar da cewa cibiyoyin lafiya suna da isasshen magani kuma a shirye suke don magance matsalolin cizon macizai cikin gaggawa, tare da tabbatar da ci gaba da samar da magani ga al’umma.

Wannan shiri na nuna jajircewar Gwamnatin Jihar Filato wajen inganta ayyukan lafiya na gaggawa, rage mace-macen da ake yi, da inganta rayuwar al’umma. Gwamnatin ta nuna aniyar ta na samar da ayyukan kiwon lafiya masu inganci ga al’ummar jihar.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

  • YAHAYA SHUAIBU

    Popularly known as Yahmis Yahaya a Media Technology Professional and Journalist with extensive experience in digital media, broadcasting technology, streaming services, and online publishing. He specializes in leveraging technology to enhance news production, content distribution, and audience engagement. As the Founder of Hausa360 Media and a media technology practitioner, he is passionate about digital journalism, technology reporting, media innovation, and the use of emerging technologies to strengthen information access and public communication.

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker