BellBank Ta Kai Karar CBN Kan Soke Lasisi

BellBank ta kalubalanci matakin da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya dauka na soke lasisin ta. A cikin wata sanarwa, wanda ya kafa bankin, Bello Kano, ya ce bankin bai yarda da dalilan da hukumar ta bayar ba. Bankin ya fara shigar da karar a hukumance.
A cikin sakon da aka aika wa abokan hulda, BellBank ta tabbatar wa abokan cinikinta cewa tana daukar matakin shari’a. Bankin ya ce: “Mun fara daukar matakin shigar da korafi a hukumance, wato appeal ga hukumomin da abin ya shafa domin a sake duba lamarin.” Wannan domin kalubalantar hukuncin hukumar.
BellBank ta nuna godiya ga abokan huldarta kan damuwarsu da ci gaba da goyon baya. Wanda ya kafa bankin ya ce bankin ya kuduri aniyar magance matsalar kuma zai sanar da abokan cinikinsa duk wani ci gaba. Bankin na godiya da amincewar da aka ba shi.





