Duniya

Harin da aka kai Iran ya lalata wurin bautar Yahudawa

Harin jirage marasa matuƙa da aka kai a Tehran ya lalata wani wurin bautar Yahudawa, yayin da aka ji karar fashe-fashe daga sassa daban-daban na babban birnin Iran.

Rahotanni sun ce an samu fashewa a yankin Parchin da wasu unguwanni a yamma da kudu na Tehran.

Haka kuma an samu rahotannin fashe-fashe a Qom, yayin da gwamnan Lorestan Province ya sanar da cewa an kai hari kan Khorramabad Airport.

A cewar Islamic Republic of Iran Broadcasting, wuraren da aka kai wa hari a Tehran sun haɗa da Tehranpars da Saadatabad, da kuma Mehrabad International Airport, tare da wasu wuraren kasuwanci da ke kan Babban Titin Haki da shagunan Rumi.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker