Duniya

Wa’adin da Trump ya bai wa Iran kan mashigar Hormuz ya kare yau

A yau ne wa’adin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya bai wa Iran domin ta bude mashigar Strait of Hormuz ke karewa.

A ranar Litinin da ta gabata, Trump ya yi barazanar cewa Amurka za ta kai hare-hare kan muhimman ababen more rayuwa a Iran, ciki har da tashoshin wutar lantarki da gadoji, idan har ƙasar ta ƙi buɗe mashigar.

Tun da farko dai Iran ta yi watsi da shawarar tsagaita wuta na wucin gadi, tana mai jaddada cewa za ta amince ne kawai da kawo ƙarshen yaƙin gaba ɗaya na dindindin.

A wani ɓangare kuma, jakadan Iran a Pakistan wadda ke taka rawa wajen shiga tsakani tsakanin Amurka da Iran ya yaba da ƙoƙarin Pakistan na sasanta bangarorin biyu, yana mai cewa yunƙurin dakatar da rikicin na samun wani muhimmin ci gaba.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker