Labarai

Rashin Lafiya Ta Hana Sadiya Zuwa Kotu

Tsohuwar Ministar Harkokin Jin Kai, Sadiya Umar Farouq, ba ta samu damar bayyana a gaban kotu ba sakamakon rashin lafiya da take fama da ita a kasar Egypt.

Lauyanta, Oladipo Okpesheyi, ya sanar da babbar kotun tarayya da ke Apo cewa tana karbar magani ne a Egypt, inda likitoci suka ce ba za ta iya komawa kotu ba sai bayan wasu watanni biyu.

Hukumar Economic and Financial Crimes Commission ta gurfanar da ita tare da Bashir Nura Alkali da Sani Mohammed bisa tuhume-tuhume 21 da suka hada da cin amanar aiki da karkatar da kudade.

A zaman kotun ranar Litinin, lauyan EFCC, Rotimi Jacobs (SAN), ya bukaci a ci gaba da sammacin kama Farouq saboda rashin halarta.

Alkalin kotun, Jude Onwuegbuzie, ya nuna damuwa kan jinkirin shari’ar tare da gargadin daukar karin mataki idan ba ta bayyana a zama na gaba ba.

Kotun ta dage sauraron karar zuwa ranar 8 ga Yunin 2026 domin fara karanta tuhume-tuhumen.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker