Labarai

NAHCON ta kammala jigilar mahajjatan Nijeriya 2026 Saudiyya

Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON ta sanar da kammala jigilar maniyyatan Nijeriya na aikin Hajjin shekarar 2026 zuwa kasar Saudiyya.

Hukumar ta bayyana cewa an kammala aikin ne bayan tashin jirgi na karshe da kamfanin jiragen sama Max Air ya yi daga filin jirgin saman Gusau, inda ya dauki maniyyatan jihar Zamfara zuwa kasa mai tsarki.

Rahotanni daga jaridar Daily Trust sun bayyana cewa NAHCON ta ce an gudanar da tashin jirage 98 cikin tsawon kwanaki 18 kacal, inda aka kammala jigilar dukkan mahajjata cikin nasara.

Nijeriya ta kuma samu adadin guraben maniyyata 50,000 domin aikin Hajjin bana.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker