Duniya

Makaman Rokar Iran Sun Fada Tsakiyar Isra’ila

Wasu makaman roka da Iran ta harba sun fada a yankuna masu cunkoson jama’a a tsakiyar Isra’ila da safiyar yau Asabar.

Rahotanni sun ce ma’aikatan agajin gaggawa sun garzaya wuraren da abin ya faru a biranen Petah Tikva da Ramat Gan domin duba halin da ake ciki da kuma taimaka wa waɗanda abin ya shafa.

A halin da ake ciki, hare-haren da Iran ke kaiwa a yankin Gabas ta Tsakiya na ci gaba, inda ma’aikatar harkokin cikin gida ta Bahrain ta buƙaci jama’a su nemi mafaka bayan kararrawar gargadi ta tashi a sassa daban-daban na ƙasar.

Rahotanni sun kuma nuna cewa wani wurin sarrafa iskar gas ya kama da wuta a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa sakamakon tarkacen wasu abubuwa da suka faɗo daga sama.

Haka kuma a Kuwait, an ce wasu hare-hare sun lalata wasu muhimman cibiyoyi da suka haɗa da tashoshin samar da lantarki, cibiyoyin tace ruwan sha da kuma matatar mai.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker