Labarai

Majalisar Wakilan Amurka Ta Gabatar da Kuduri Kan Zargin Cin Zarafin Addini a Najeriya

Kwamitin Majalisar Wakilan Amurka ya gabatar da wani kuduri da ke neman a dauki mataki kan zargin musguna wa Kiristoci da kuma ayyukan wasu kungiyoyin yan bindiga a Najeriya.

Kudirin, mai taken “Nigeria Religious Freedom and Accountability Act,” ya bukaci Sakataren Harkokin Wajen Amurka ya rika gabatar wa kwamitocin harkokin wajen majalisa rahoto duk shekara kan matakan da ake dauka domin magance zargin take hakkin addini a Najeriya.

Haka kuma, kudurin ya nemi a tantance yiwuwar ayyana wasu kungiyoyi da ake dangantawa da “makiyaya Fulani” a matsayin kungiyoyin ta’addanci na kasashen waje. Bugu da kari, ya bukaci a sanya takunkumi kan wasu mutane da ake zargi da hannu a cin zarafin Kiristoci.

Domin kudurin ya zama doka, dole ne ya samu amincewar duka majalisun dokokin Amurka.

Wannan mataki na zuwa ne bayan Amurka ta sanar da shirin tura sojoji 200 zuwa Najeriya domin horas da sojojin kasar kan dabarun yaki da masu tayar da kayar baya. Ana sa ran za su iso cikin makonni masu zuwa, inda za su hadu da wata karamar tawaga da aka riga aka tura a baya.

Kakakin rundunar sojin Najeriya, Janar Samaila Uba, ya tabbatar da shirin ga BBC, yana mai cewa hakan ya biyo bayan gayyata da bukatar gwamnatin Najeriya, kuma ya yi daidai da shawarwarin kwamitin hadin gwiwar tsaro tsakanin Amurka da Najeriya.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker