Tsaro

Benue: Mutane 24 Sun Mutu a Haren Haren Karamar Hukumar Kwande

Adadin mutanen da suka mutu a hare-haren da aka kai kan wasu kauyuka a Turan da ke yankin Jato Aka na karamar hukumar Kwande a Jihar Benue ya kai mutane 24, bayan da aka gano karin gawarwaki a yayin binciken da aka gudanar da safiyar ranar Asabar.

Mazauna yankin sun ce hare-haren, wanda ake zargin yan bindiga masu dauke da makamai ne suka kai, sun faru ne a ranar Alhamis inda suka kai hari kan kauyen Mbaav a gundumar Mbadura da kuma wasu matsugunai da ke gundumar Yaav a cikin karamar hukumar.

Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Karu Bayan Bincike

Rahotannin farko sun nuna cewa mutane 16 ne suka mutu bayan hare-hare biyu da aka kai da safe da kuma da daddare a kauyukan da abin ya shafa.

Sai dai daga bisani, kungiyoyin bincike na cikin gida sun gano karin gawarwaki a wasu wurare kusa da yankin.

Tsohon Supervisory Councillor na Kwande LGA, Akerigba Lawrence, ya tabbatar da gano karin wadanda suka mutu yayin aikin bincike da ceto.

Wasu daga cikin gawarwakin an jefa su cikin kogi. An gano guda daya a safiyar yau, wanda ya sa jimillar wadanda suka mutu ta kai 24, in ji shi.

Majiyoyin al’umma sun bayyana cewa an riga an gano wasu daga cikin wadanda suka mutu daga kauyen Mbaav, yayin da wasu daga kauyukan gundumar Yaav su ma aka tabbatar da mutuwarsu. Sai dai har yanzu ana ci gaba da gano wasu gawarwaki yayin da bincike ke gudana.

Wadanda Suka Jikkata Na Karbar Magani

Akalla mutane shida da suka jikkata a hare-haren na samun kulawar likitoci a wani asibiti da ke kusa da yankin.

A halin yanzu mazauna yankin da kungiyoyin bincike suna ci gaba da duba dazuka da bakin koguna domin gano ko akwai karin gawarwaki, saboda ana fargabar cewa adadin wadanda suka mutu na iya karuwa.

Shugabannin Siyasa Sun Yi Allah wadai

Hare-haren sun jawo kakkausar suka daga shugabannin jam’iyyar All Progressives Congress a jihar.

Shugaban jam’iyyar a Benue, Austin Agada, ya bayyana harin a matsayin ta’addanci mara imani, a wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar Morgan Ihomun ya fitar.

Ya kuma bukaci jami’an tsaro da su gaggauta kamo wadanda suka aikata laifin domin su fuskanci hukunci.

Gwamna Alia Ya Yi Alkawarin Kara Tsaurara Tsaro

Shi ma Hyacinth Alia, gwamnan Jihar Benue, ya yi Allah wadai da kisan, yana mai cewa harin ba shi da dalili kuma ba za a lamunta da shi ba.

Gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasu tare da tabbatar wa al’ummar Kwande LGA cewa gwamnatinsa za ta kara karfafa ayyukan tsaro domin kamo masu hannu a lamarin da kuma dawo da zaman lafiya a yankin.

Alia ya kuma bayyana cewa an tura jami’an tsaro sama da 400 zuwa Jato Aka da sauran kauyukan da ke kusa, amma ya amince cewa akwai bukatar daukar karin matakai domin kawo karshen hare-haren da ke maimaituwa a yankin.

Mahukunta sun ce har yanzu aikin tsaro da bincike na ci gaba, domin tabbatar da zaman lafiya da kuma hana sake aukuwar irin wannan tashin hankali a yankin.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker