Labarai

An tallafawa Yara Masu Zanga Zangar Yinwa da Tsadar Rayuwa Da Naira Miliyan 2

Jama’a Sun Tallafawa Yara Yan Kano Masu Zanga-Zangar Yinwa da Tsadar Rayuwa Da Naira Million 2

A yau Laraba Bar. Abba Hikima lauyan Al’umma da kare hakkin dan Adam ya sanar da samun taimako daga jama’a ga ƙananan yara waɗanda aka kama domin gudanar da zanga-zangar Yinwa da Tsadar Rayuwa da ya addabi ƙasa. Wannan taimako ya biyo bayan yanci da suka samu daga tsarewar da aka yi musu bayan sun shaki iskar yanci.

Mutane da dama, ciki har da manyan malamai, da Mawaka, sun tallafa wa waɗannan yara domin tabbatar da suna da wani tallafi wajen sake rayuwa. Wasu sun bayar da gudummawar miliyoyi, yayin da masu karamin karfi suma suka bayar da nasu guduma ta hanyar turawa asusun Banki na A. A. Hikima & Co. dake Jaiz wanda Bar. Abba Hikima ke Jagoranta.

Daga cikin waɗanda suka bayar da tallafin akwai Prof. Ibrahim Maqari da ya bayar da N1,000,000 da kuma Alhaji Naziru Sarkin Waka wanda shima ya bada tallafin N1,000,000 ta hannun wakilinsa. Sauran sun hada da Hajiya Samira Ado da Muhammad Abdullahi Sulaiman da dai sauran ‘yan ƙasa masu kishin al’umma.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

  • YAHAYA SHUAIBU

    Popularly known as Yahmis Yahaya a Media Technology Professional and Journalist with extensive experience in digital media, broadcasting technology, streaming services, and online publishing. He specializes in leveraging technology to enhance news production, content distribution, and audience engagement. As the Founder of Hausa360 Media and a media technology practitioner, he is passionate about digital journalism, technology reporting, media innovation, and the use of emerging technologies to strengthen information access and public communication.

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker