Labarai

Zulum: Mun rufe kasuwar Jilli shekaru biyar da suka wuce

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta rufe kasuwar Jilli tun shekaru biyar da suka gabata, sakamakon zargin cewa ta zama mafakar ƴan ta’adda.

Zulum ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa yayin da yake mayar da martani kan rahotannin wani harin sama da ake zargin rundunar sojin saman Najeriya ta kai, wanda aka ce ya yi sanadin mutuwar sama da mutum 50 a ranar Asabar.

Ya ce an riga an rufe kasuwar Jilli da kuma ta Gazabure tun da dadewa, yana mai jaddada cewa matakin ya kasance domin dalilan tsaro.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Labarai masu alaƙa

Duba
Close
Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker