Har Yanzu Nasir El-Rufai na Hannun EFCC

Mai bai wa tsohon gwamnan Kaduna State shawara kan harkokin yada labarai, Muyiwa Adekeye, ya bayyana cewa har yanzu El-Rufai yana tare da jami’an hukumar EFCC.
Adekeye ya ce tsohon gwamnan ya amsa gayyatar da hukumar ta aika masa a ranar Litinin, inda ya je ya ba da amsa ga tambayoyin da aka yi masa kamar yadda aka buƙata.
Ya kara da cewa tattaunawar da aka yi tsakanin El-Rufai da jami’an hukumar ta kasance mai amfani kuma cikin fahimta. A cewarsa, lauyan tsohon gwamnan ya lura cewa jami’an da suka karbe shi sun nuna kwarewa da mutunci wajen gudanar da aikinsu.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa har yanzu El-Rufai yana tare da jami’an hukumar, ba tare da an bayyana lokacin da za a sallame shi ko kuma ko an kammala tambayoyin da ake masa ba.
Hukumar EFCC ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan batun ba zuwa lokacin hada wannan rahoto.
El-Rufai, wanda ke daga cikin manyan jagororin adawa a African Democratic Congress (ADC) da ke shirin kalubalantar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na All Progressives Congress (APC) a zabe mai zuwa, ya zargi gwamnati da matsa wa ‘yan adawa lamba ta hanyar binciken rashawa.
Ya kuma ce an riga an kama wasu daga cikin mutanen da suka yi aiki tare da shi a Kaduna, yana mai cewa tun da farko yana tsammanin za a gayyace shi, abin da yanzu ya tabbata.





