Labarai
Tinubu Ya Nada Amb. Ismail Abba Yusuf a Matsayin Shugaban NAHCON

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Ambasada Ismail Abba Yusuf a matsayin sabon Shugaba/Kwamishinan Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON).
Nadin nasa na jiran amincewar Majalisar Dattawa kamar yadda sashe na 3(2) na Dokar NAHCON ta shekarar 2006 ya tanada.
Shugaba Tinubu ya aike da wasika ga Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, inda ya bukaci a gaggauta tabbatar da nadin Ambasada Yusuf domin maye gurbin Farfesa Abdullahi Usman, wanda ya yi murabus a wannan mako bayan shafe kimanin watanni 14 a kan mukamin.
Ambasada Ismail Abba Yusuf gogaggen jami’in diflomasiyyar Nijeriya ne, wanda ya taba zama Jakadan Nijeriya na musamman kuma cikakken wakili a Jamhuriyar Turkiya daga shekarar 2021 zuwa 2024.





