Labarai

Zulum: Matsin Lamba a Sambisa Ne Ya Jawo Harin Ta’addanci a Ngoshe

Gwamnan jahar Borno Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa harin ta’addancin da aka kai a garin Ngoshe ya faru ne sakamakon matsin lambar da sojoji suka yi wa yan ta’adda a dajin Sambisa, wanda ya tilasta musu barin mafakarsu.

Gwamnan ya yi wannan bayani ne yayin da ya kai ziyarar jajantawa ga al’ummar yankin a karamar hukumar Gwoza, bayan wani mummunan hari da yan ta’adda suka kai wanda ya yi sanadin mutuwar fararen hula da sojoji, tare da sace wasu mutane da lalata gidaje da dukiyoyi.

Gwamna Ya Jajanta wa Iyalin Wadanda Suka Rasa Rayukansu

Yayin ziyarar, Gwamna Zulum ya nuna alhininsa ga iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu sakamakon harin.

Mun zo nan ne domin jajanta wa al’ummar Ngoshe da suka rasa yan uwansu sakamakon wannan lamari mara dadi da ya faru ranar Talata. Lamarin abin takaici ne matuka, kuma zukatanmu na tare da duk wanda abin ya shafa, in ji Zulum.

Ya tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnati za ta dauki matakan gaggawa domin dawo da tsaro da kuma tallafa wa wadanda harin ya shafa.

Haka kuma ya ce rundunar sojan najeriya za ta yi duk mai yiwuwa domin ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a harin.

Yan Ta’adda Sun Fito Daga Sambisa

Gwamnan ya bayyana cewa ci gaba da hare-haren da sojoji ke kai wa a cikin dajin Sambisa ne ya tilasta wa yan ta’adda barin maboyarsu, lamarin da ya sa suka kai hare-hare kan garuruwa da kauyukan da ke kusa da su.

A halin yanzu ana gudanar da manyan ayyukan soji a dajin Sambisa. Abin da ya faru a nan ya faru ne sakamakon matsin lambar da aka yi wa yan ta’addan a maboyarsu, wanda ya sa suka kai hare-hare kan al’ummomin da ke kusa, in ji shi.

Kira Ga Kara Karfin Ayyukan Soji

Zulum ya kuma yi kira ga sojojin Najeriya da gwamnatin tarayya da su kara karfafa ayyukan tsaro a yankin tsaunin Mandara , wanda ya bayyana a matsayin daya daga cikin manyan wuraren da yan ta’adda ke fakewa.

Ya ce galibin yan ta’addan na saukowa daga tsaunukan ne domin kai hare-hare kan garuruwa da kauyuka a yankin Gwoza.

Har Yanzu Ba a Tabbatar da Yawan Wadanda Suka Mutu Ba

Gwamnan ya ce har yanzu ba a kammala tantance ainihin yawan mutanen da suka rasa rayukansu ba, domin jami’an tsaro na ci gaba da gudanar da bincike da tantance barnar da aka yi.

Sai dai ya tabbatar da cewa mutane da dama sun mutu yayin da wasu kuma aka yi garkuwa da su a harin.

Tallafin Gaggawa Ga Wadanda Suka Rasa Matsuguni

A matsayin matakin agaji na gaggawa, gwamnatin jihar Borno ta fara raba kayan tallafi ga wadanda harin ya shafa tare da kafa wuraren dafa abinci na musamman domin samar da abinci ga mutanen da suka rasa matsugunansu.

A yanzu haka za mu fara rabon kayan abinci ga wadanda abin ya shafa, sannan kuma mun ba da umarnin kafa wuraren dafa abinci domin kowa a wannan al’umma ya samu abinci daga wuri guda, in ji gwamnan.

Zulum Ya Duba Barnar da Aka Yi a Konduga

A yayin da yake gudanar da wadannan ziyarce-ziyarcen, Gwamna Zulum ya kuma kai ziyara a garin Konduga domin duba gidajen da yan kungiyar Boko Haram suka kona a wani hari da suka kai.

Tun da farko ma gwamnan ya kai ziyara a garin Pulka, inda ya gana da iyalan wadanda suka rasa rayukansu a hare-haren, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin takaici matuka.

Gwamnati Ta Kuduri Aniyar Maido da Zaman Lafiya

A karshe, Gwamna Zulum ya bukaci al’ummar yankin da su kasance masu bin doka da oda yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da gudanar da ayyukan su.

Ya kuma jaddada kudurin gwamnatin jihar na tabbatar da dawowar zaman lafiya a dukkan fadin Borno.

Ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da dorewar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jiharmu. Da yardar Allah, tare da ci gaba da ayyukan soji da hadin kan dukkan bangarori, za mu shawo kan wannan kalubale kuma zaman lafiya zai dawo ƙasar mu, in ji gwamnan.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga
WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter
Facebook: Hausa360 Facebook
Instagram : @Hausa360
YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Labarai masu alaƙa

Back to top button

Adblock Detected

Please enable adblocker