Kai Tsaye | Rasuwar Mahaifiyar Nasiru El-Rufai
Kai Tsaye | Rasuwar Mahaifiyar Nasiru El-Rufai
Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye dangane da rasuwar mahaifiyar Malam Nasiru El-Rufai
Atiku Abubakar: Rasuwar Hajiya Umma El-Rufai abin tashin hankali
Atiku ya tuna da marigayiyar a matsayin mace mai imani da hidima ga al’umma, ya kuma roki Allah ya bai wa iyalanta hakuri, Allah kuma yajikanta da rahama.
Ya kara da cewa ya ce rasuwar ta girgiza zuciya, amma rasuwarta ranar Juma’a abin sanyaya zuciya ne ga iyali.
Mutuwar Mahaifiyar El-Rufai ya girgizani inji Nuhu Ribado
Nuhu Ribadu ya wallafa a shafin sa cewa mutuwar mahaifiyar Malam Nasiru El-Rufai ya girgizani domin rayuwa da ita a matsayin uwa jajirtaciya.
Ta’aziyya ta rikide zuwa muhawara
Ra’ayoyin Jama’a Sun Rabu Kashi: Yayin da ake jimamin rasuwar Hajiya Umma El-Rufai, mabiya shafukan Gwamna Uba Sani sun mayar da martanin da sakon ta’aziyyar da Gwamna Uba Sani yayi kana cewa thier mother hakan ya jawo cece-kuce a tsakanin al’umma.
👉 Wasu na kira ga hadin kai, wasu kuma na ganin siyasa ta shigo ciki.
Gwamnar Kaduna Uba Sani Yayi Taaziyya Ga Iyalan El-Rufai
Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayyana alhininsa bisa rasuwar mahaifiyar tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai A shafun sa na Facebook
A cikin sakonsa, ya ce yana mika ta’aziyyarsa ga El-Rufai da daukacin iyalansa bisa wannan babban rashi.
Ya bayyana marigayiya, Hajiya Umma El-Rufai, a matsayin mace mai tausayi, tawali’u da kuma kyawawan dabi’u, wacce ta rayu tana taimakon al’umma tare da bayar da shawarwari masu amfani.
Gwamnan ya kara da cewa marigayiyar ta kasance ginshiki wajen hada kan jama’a da kuma yada kyawawan dabi’un addini da hakuri.
👉 Ya yi addu’ar Allah ya gafarta mata kura-kuranta, ya karbi ayyukanta na alheri, ya kuma saka ta da Aljannatul Firdaus.
🙏 Ya kuma roki Allah ya bai wa iyalanta hakurin jure wannan babban rashi.
Hajiya Fatima Zarah Ahmad ta rasu a Cairo
A rahoton da muke samu yanzu Hajiya Fatima Zarah Ahmad ta rasu a Cairo bayan jinya.
Shin El-Rufai zai samu halartar jana izar Mahaifiyarsa ?
Zaku iya rubuta mana Ra’ayinku a shafukan sada zumunta na Hausa360
Acikin Awa Daya Mutane sama da dubu ashirin ( 20000 ) sun jajin ta wa Bello El-Rufai
Mutane sama da dubu shirin ( 20000 ) sun jajin ta wa Bello El-Rufai ackin a wa daya da sanarwar da yayi a shafin sa na Facebook.
Bello El-Rufai Yasanar da Rasuwar Kakarsa
Sanarwar yafito ne daga shafin dan Malam Nasiru El-Rufai, a yau Juma\'a da misalin karfe 4:45 na yamma, ya bukaci al\'umma da su tayasu da addua
Mahaifiyar Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai Ta Rasu
Rahotanni sun bayyana cewa Hajiya Umma El-Rufai ta rasu ne a ‘yan sa’o’i da suka gabata, lamarin da ya jefa iyalai da makusanta cikin jimami.