Wani matashi dan jihar Delta zai aure mata biyu a lokaci daya

Matashin dai mai suna Samson Uthuko Uloho dan jihar Delta a kudan cin Nigeria ya shirya tsaf dan auran yan mata 2 a lokaci daya.

Wanda a halin yanzun har an sa ranar auren ranar a sabar 11 ga watan April 2021 a karamar hukumar Isoko ta kudu.

Katin Gayyatar Aure



Sunayen yan matan kuwa sune Evelyn da Faith, tuni katin gayyatar daurin auren ya bazu a shafukan sada zumunta inda kowa yana tofa albarkacin bakin sa. Ga muharar shafin twitter akan wannan katin gayyatar wanda shafin wani mai suna @wakajugde ya wallafa.



Wannan batu a arewancin Nigeria abune wanda matasan arewa sun jima da yin hakan kuma ya fara zama ruwan dare sai dai kudan cin Nigeria abune bako wanda baโ€™a saba yin sa ba.

Haka zalika a addinin kirista wannan batun babban lamarine dan kuwa auren mata biyu kamar haramun ne a garesu saidai gashi shi wannan matashi zai aure mata biyu a lokaci guda.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

  • Popularly known as Yahmis Yahaya a Media Technology Professional and Journalist with extensive experience in digital media, broadcasting technology, streaming services, and online publishing. He specializes in leveraging technology to enhance news production, content distribution, and audience engagement. As the Founder of Hausa360 Media and a media technology practitioner, he is passionate about digital journalism, technology reporting, media innovation, and the use of emerging technologies to strengthen information access and public communication.

โ†‘
Exit mobile version