Trump Ya Yi Bayani Kan Tattaunawar Zaman Lafiya Da Iran

Shugaban Donald Trump ya yi karin haske kan halin da ake ciki game da tattaunawar zaman lafiya tsakanin United States da Iran.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce rikicin da ke tsakanin ƙasashen biyu da kuma toshe hanyoyin jiragen ruwan Iran na iya ƙarewa idan aka cimma yarjejeniya mai amfani.

Sai dai ya yi gargadin cewa Amurka na iya ci gaba da kai hare-haren soji kan Iran idan ba a cimma matsaya ba.

Ya kuma bayyana cewa idan Iran ta amince da dukkan sharuɗɗan da ake bukata, to rikicin zai zo ƙarshe.

Trump ya ƙara da cewa rashin cimma yarjejeniya zai iya haifar da ƙarin hare-hare da zai fi tsanani fiye da na baya, yana mai jaddada matsin lamba ga Tehran wajen shiga tattaunawa mai ma’ana.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Exit mobile version