Shugaban Donald Trump ya yi karin haske kan halin da ake ciki game da tattaunawar zaman lafiya tsakanin United States da Iran.
A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce rikicin da ke tsakanin ƙasashen biyu da kuma toshe hanyoyin jiragen ruwan Iran na iya ƙarewa idan aka cimma yarjejeniya mai amfani.
Sai dai ya yi gargadin cewa Amurka na iya ci gaba da kai hare-haren soji kan Iran idan ba a cimma matsaya ba.
Ya kuma bayyana cewa idan Iran ta amince da dukkan sharuɗɗan da ake bukata, to rikicin zai zo ƙarshe.
Trump ya ƙara da cewa rashin cimma yarjejeniya zai iya haifar da ƙarin hare-hare da zai fi tsanani fiye da na baya, yana mai jaddada matsin lamba ga Tehran wajen shiga tattaunawa mai ma’ana.
