Gwamnatin Kano Ta Karbi Bakuncin Tawagar Ofishin Jakadancin Birtaniya

Gwamnatin Jihar Kano ta karbi bakuncin wata tawaga daga Babban Ofishin Jakadancin Birtaniya da ke Najeriya domin ƙarfafa alaƙar haɗin gwiwa da ci gaba tsakanin ɓangarorin biyu.

Tawagar wadda Ms. Cynthia Rowe, shugabar sashen haɗin gwiwar raya ƙasa ta ofishin jakadancin Birtaniya, ta jagoranta ta kai ziyarar ban girma ne domin duba ayyukan haɗin gwiwa da ake gudanarwa ƙarƙashin tsarin UK-Kano Mutual Accountability Framework.

A yayin ziyarar, an wakilci Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, inda aka tattauna muhimman fannoni da suka haɗa da gyaran tsarin shugabanci, ilimi, lafiya, bunƙasa tattalin arziki, ƙarfafa cibiyoyi da kuma haɗa kowa cikin harkokin ci gaba.

Bangarorin biyu sun jaddada muhimmancin ci gaba da haɗin gwiwa domin samar da ci gaba mai ɗorewa da inganta rayuwar al’ummar jihar Kano.

Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin ƙarfafa dangantaka tsakanin gwamnatin Kano da ƙasashen ƙetare wajen samar da ayyukan raya ƙasa da ci gaban al’umma.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Exit mobile version