CUPS Ta Kaddamar da Sabon Logo

Kungiyar Citizens United for Peace and Stability (CUPS) ta fitar da sabon tambarinta wanda aka ce ya lashe gasar zane na kungiyar. Dr. Idris Ahmed, shugaban kungiyar, ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau, 9 ga watan Janairu, 2025.

Bayan nazari mai zurfi da aka gudanar kan tambarin da aka gabatar, kungiyar ta bayyana cewa tambarin da matashin mai zane, Adamu Muazu Mijinyawa, ya kirkira, shi ne ya samu nasara. An bayyana cewa bai yi amfani da wata fasahar artificial intelligence (AI) wajen kirkirar wannan tambari ba.

CUPS ta yi kira ga mabiya da masu goyon baya da su yi amfani da wannan tambarin wajen tallata sunan kungiyar a rubuce-rubucensu da kuma kafafen sada zumunta.

Kungiyar ta ce kare martaba da bunkasa sunan CUPS yana da matukar muhimmanci wajen cimma burin ceton Arewa da al’ummarta. Dr. Idris ya ce:

“Muna rokon Allah Ubangiji ya albarkaci wannan kuduri da nasara mai tarin yawa. Amin, Ya Rabbi.”

Ana fatan wannan sabon tambari zai kara fito da matsayin CUPS a matsayin wata kungiya mai karfin gwiwar kawo zaman lafiya da daidaito a yankin Arewa da ma duniya baki daya.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

  • Popularly known as Yahmis Yahaya a Media Technology Professional and Journalist with extensive experience in digital media, broadcasting technology, streaming services, and online publishing. He specializes in leveraging technology to enhance news production, content distribution, and audience engagement. As the Founder of Hausa360 Media and a media technology practitioner, he is passionate about digital journalism, technology reporting, media innovation, and the use of emerging technologies to strengthen information access and public communication.

Exit mobile version