APC ta tsawaita sayar da fom din takara zuwa Litinin

All Progressives Congress (APC) ta sanar da tsawaita lokacin sayar da fom din takara da bayyana niyya daga ranar Asabar, 2 ga Mayu, 2026 zuwa daren Litinin, 4 ga Mayu, 2026.

Jam’iyyar ta kuma matsar da ranar mika fom daga Asabar zuwa Talata, 5 ga Mayu, 2026, yayin da za a gudanar da tantance ‘yan takara a ranar Laraba, 6 ga Mayu, 2026.

Mataimakin sakataren yada labarai na jam’iyyar, Duro Meseko, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a sakatariyar APC ta kasa a Abuja.

Ya ce an dauki matakin ne sakamakon hutun gwamnati da za a yi ranar Juma’a, domin bai wa masu neman takara damar sayen fom dinsu.

A cewarsa, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar (NWC) ne ya amince da sauyin, bayan korafe-korafe da aka samu daga jihohi daban-daban.

Meseko ya kara da cewa matakin zai bai wa dukkan masu sha’awar takara damar shiga cikin tsarin ba tare da wata matsala ba.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Exit mobile version