Wasu masu neman takarar Majalisar Wakilai da Majalisar Dokokin Jihar Kano a Jam’iyyar ADC sun barranta kansu daga takardar tuhumar da aka aika wa Kwamared Muhammad Tukur Warawa. Takardar ta zargi Hajiya Naja’atu Muhammad da karbar kudi domin ba masu neman takara damar tsayawa takara.
Shugaban ƙungiyar ADC Kano State Support Group, Hon. Muhammad Yusuf Babba Dan Agundi, ne ya sanya wa hannu a ranar Laraba 24 ga Yunin 2026. Takardar ta ce wasu daga cikin masu neman takara 44 da aka ambata sun ce ba su bai wa Hon. Sa’idu Nakowa izinin wakiltarsu ba.
Ƙungiyar ta bukaci Barrista Mubarak Muhammad na Definite Edge Consultants da ya cire sunayen wadanda abin ya shafa. Ta ce za su dauki matakin shari’a idan ba a cire sunayensu cikin sa’o’i 24 ba.
Wannan na kara fito da tsamin dangantakar da ke tsakanin ɓangaren Hajiya Naja’atu Mohammed da tsagin Hon. Musa Ungogo. Wannan dai tsohuwa da sabuwar ADC ce a Kano.
Rikicin na ADC Kano na kara tsananta yayin da ake shirin zaɓen 2027. Bangarorin biyu suna fafutukar neman goyon baya. Sai a ga ko za a samu sulhu tsakaninsu.

