Saudiya Ta Fitar Da Ranakun Arfa Da Sallah

Mahukuntan kasar Saudiyya sun sanar da ranakun da za a gudanar da hawan Arfa da kuma bikin Babbar Sallah na bana bayan kammala duba jinjirin watan ZulHijjah.

A cewar sanarwar da aka fitar, ranar 26 ga watan nan za ta kasance ranar Arfa, yayin da ranar 27 za ta kasance ranar Babbar Sallah ga al’ummar Musulmi.

Sanarwar ta zo ne bayan tabbatar da ganin watan a wasu sassan kasar.

Musulmai daga sassa daban-daban na duniya na ci gaba da shirye-shiryen gudanar da ibadun Hajji da kuma bukukuwan Sallah, yayin da mahajjata ke ci gaba da taruwa a birnin Makkah domin gudanar da manyan ibadun aikin Hajji.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Exit mobile version