Supreme Court of Nigeria ta soke umarnin kotun ɗaukaka ƙara da ya tanadi komawa yadda aka fara (status quo ante bellum) a rikicin shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).
Hukuncin ya dawo da shugabancin bangaren David Mark bayan cire shi daga rajista da Independent National Electoral Commission (INEC) ta yi.
A hukuncin da aka yanke baki daya ranar Alhamis, kwamitin alkalai biyar karkashin jagorancin Mai Shari’a Mohammed Lawal Garba ya bayyana cewa umarnin kotun ɗaukaka ƙara bai dace ba.
Kotun Ƙolin ta kuma ce daukaka ƙarar da aka shigar kan batun hurumi ba ta bi ka’ida ba, domin an shigar da ita ne kan umarnin wucin gadi ba tare da samun izini daga kotun ɗaukaka ƙara ba.
