Kotu ta cire zargin ta’addanci daga tuhumar Malami

Gwamnatin Tarayya ta sauya zarge-zargen da take yi wa tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, tare da ɗansa Abdul’aziz, inda aka cire zargin ɗaukar nauyin ta’addanci.

A zaman kotu na ranar Laraba, wakilin hukumar DSS, Akinlolu Kahinde, ya sanar da kotu cewa an sauya tuhumar, tare da maye gurbin wasu daga cikin zarge-zargen.

Daga cikin sauye-sauyen akwai cire zargin mallakar makamai.

Lauyan Malami, Shu’aibu Aruwa, ya tabbatar da cewa wanda yake karewa ya amince da sabbin tuhumomin da aka gabatar bayan an karanta su a kotu.

Karanta: Hukumar DSS ta bude shafukan sada zumunta dan yin aiki

Tun da farko dai Malami ya musanta dukkan zarge-zargen da aka yi masa.

Kotun ta ɗage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 26 ga watan Mayu da kuma 15 ga watan Yuni.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Exit mobile version