Isra’ila Ta Kashe Kwamandan Hezbollah A Beirut

Wata majiya da ke kusa da Hezbollah ta tabbatar da cewa an kashe ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar a wani hari da Israel ta kai a kudancin birnin Beirut na Lebanon a ranar Laraba.

Rahotanni sun bayyana cewa wannan ne hari na farko da aka kai a yankin cikin kusan wata guda.

Majiyar ta bayyana sunan kwamandan da aka kashe a matsayin Malek Ballout, wanda ake zargin shi ne ke jagorantar ayyukan rundunar Radwan ta kungiyar Hezbollah.

Karanta: Isra’ila Ta Janye Sunan Ministan Iran Daga Jerin Hari

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana cewa shi da kansa ne ya bayar da umarnin kai harin kan kwamandan kungiyar.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Exit mobile version