Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijar ta samu nasarar kama muggan kwayoyi da darajarsu ta kai CFA biliyan 8 a yankin Tawa da ke arewacin kasar.
Rahotanni sun ce an kama mutane shida a Yamai da Tawa, waɗanda ake zargi da hannu a safarar miyagun kwayoyin.
A wata tattaunawa kan lamarin, shugaban wata kungiyar matasa a jihar Tawa, Hamisou Ilyassou Issa, ya yi tsokaci kan nasarar da hukumomi suka samu wajen dakile wannan fatauci.
Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group
Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.
