Jami’an hukumar tsaro ta DSS sun sake kama tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, jim kadan bayan wata babbar kotu da ke Abuja ta amince da bayar da belinsa kan wasu zarge-zarge da ake yi masa.
Lamarin ya jawo ceceku ce a tsakanin magoya bayansa da wasu yan siyasa, yayin da ake jiran karin bayani daga hukumomin tsaro dangane da dalilin sake cafke shi bayan samun beli daga kotu.
Rahotanni sun bayyana cewa an dauke shi ne daga harabar kotun bayan kammala shari’ar ranar.
Tun farko, kotun ta bayar da belinsa kan kudi Naira miliyan 100 tare da sharadin samun wanda zai tsaya masa daga yankunan Maitama ko Asokoro a Abuja.
Sai dai bayan fitowarsa daga kotun, jami’an DSS suka sake tsare shi domin ci gaba da bincike kan zarge-zargen da ake yi masa.
Lamarin ya jawo ceceku ce a tsakanin magoya bayansa da wasu yan siyasa, yayin da ake jiran karin bayani daga hukumomin tsaro dangane da dalilin sake cafke shi bayan samun beli daga kotu.
