Amurka Da China Sun Hada Kai Kan Iran

Kasashen Amurka da China sun bayyana matsaya guda kan hana Iran mallakar makamin nukiliya, yayin da rikicin siyasa da tattaunawar diplomasiyya ke ci gaba a duniya.

Rahotanni sun nuna cewa shugabannin kasashen biyu sun jaddada muhimmancin tabbatar da cewa Iran ba ta samu damar kera makamin nukiliya ba, saboda barazanar da hakan ka iya haifarwa ga zaman lafiya da tsaron duniya.

A yayin tattaunawar, bangarorin biyu sun kuma nuna bukatar ci gaba da amfani da hanyoyin sulhu da diflomasiyya wajen warware matsalar shirin nukiliyar Iran maimakon daukar matakan da za su kara tayar da rikici.

Masu sa ido kan harkokin siyasa na ganin wannan matsaya ta bai daya tsakanin manyan kasashen biyu na iya taimakawa wajen rage tashin hankali tare da karfafa kokarin kasashen duniya na hana yaduwar makaman nukiliya.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Exit mobile version