Al’ummar Ariko sun musanta ikirarin Sojin Najeriya kan ceto masu ibada

Al’ummar garin Ariko da ke karamar hukumar Kachia a jihar Kaduna State sun musanta rahoton Nigerian Army da ke cewa dakarunta sun ceto masu ibada 31 da ƴanbindiga suka yi garkuwa da su.

An sace mutanen ne a lokacin da suke tsaka da ibada a wasu majami’u biyu a garin Ariko ranar Lahadi da ta gabata.

Rahotannin kafafen yada labarai a Najeriya sun ambato rundunar sojin kasar tana cewa dakarunta sun yi gumurzu da ƴanbindiga a cikin daji, inda daga bisani suka ceto mutanen sa’o’i kaɗan bayan an sace su.

Sai dai shugaban ƙungiyar al’ummar Kuturmi, Dakta David Joseph Ariko, ya musanta wannan iƙirari a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.

Author

Exit mobile version