Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Katsina ta yi kakkausar suka kan sabbin hare-haren yan bindiga da ke faruwa a yankuna daban-daban na jihar.
Jam’iyyar ta bayyana cewa kashe jami’an tsaro da fararen hula abin damuwa ne kwarai, tare da cewa lamarin ya wuce matakin da za a yi shiru akai.
ADC ta bukaci gwamnati da hukumomin tsaro su kara kaimi wajen dakile ayyukan yan bindiga, tare da samar da tsare-tsare masu dorewa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.
Hare-haren yan bindiga a Arewa maso Yamma na ci gaba da zama babban kalubale, inda al’ummomi da dama ke fuskantar matsalar tsaro, garkuwa da mutane da kashe-kashe.
Jam’iyyar ta jaddada cewa dole ne a dauki matakan gaggawa domin kawo ƙarshen wannan matsala kafin ta kara ta’azzara.
