Ofishin Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (NSA) ya musanta zargin cewa ya sayo ko ya shigo da sinadarin thallium sulphate, wani sinadari mai tsananin guba wanda ba shi da launi ko wari kuma zai iya kashe mutum cikin dan kankanin lokaci.
Musanta lamarin ya biyo bayan wata wasika da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya aike wa Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu, mai kwanan wata 30 ga Janairu, 2026.
A cikin wasikar, El-Rufai ya ce wasu bayanai da suka samu daga shugabannin adawa na nuna cewa ofishin NSA ya sayo kusan kilogram 10 na thallium sulphate daga wani mai sayarwa a Poland.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa an mika batun ga Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Kasa (DSS) domin gudanar da cikakken bincike. Haka kuma za a gayyaci El-Rufai da duk masu bayanai masu alaka da zargin domin su gabatar da hujjoji.
Abubuwan da ke cikin wasikar El-Rufai
A wasikarsa, El-Rufai ya bayyana zargin a matsayin abin damuwa ga jama’a, yana mai cewa sinadaran thallium na daga cikin abubuwan da ake takaita su sosai saboda tsananin gubarsu.
Ya nemi a fayyace muhimman bayanai kamar:
- manufar sayen sinadarin da yadda za a yi amfani da shi,
- sunan kamfanin da aka siya daga gare shi da kuma izinin shigo da shi,
- adadi da karfinsa,
- matakan ajiya da tsaro bayan shigowarsa kasa,
- kulawar hukumomi kamar National Agency for Food and Drug Administration and Control (NAFDAC) da Nigeria Centre for Disease Control (NCDC),
- da kuma ko an yi nazarin hadarin lafiyar jama’a da matakan rage illa.
Ya ce ya yi tambayoyin ne domin tabbatar da bin ƙa’idoji, tsaro da gaskiya, yana mai cewa amincewar jama’a ga hukumomi na ƙaruwa ne idan ana bayyana gaskiya kan irin waɗannan batutuwa.
Rikicin Ribadu da El-Rufai
Musayar kalaman na zuwa ne a daidai lokacin da dangantaka tsakanin Ribadu da El-Rufai ke ƙara dagulewa, duk da cewa a baya sun kasance abokai na kud-da-kud.
Dukansu sun yi fice a lokacin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo. A wancan lokaci, Ribadu shi ne shugaban farko na Economic and Financial Crimes Commission (EFCC), yayin da El-Rufai ya rike mukamin Darakta Janar na Hukumar Kula da Kamfanonin Gwamnati kafin daga bisani ya zama minista.
Dangantakarsu ta fara tsami ne a 2011 lokacin da jam’iyyar ACN ta tsayar da Ribadu takarar shugaban kasa matakin da El-Rufai bai goyi baya ba, inda ya marawa tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari baya a wancan zaben.
