Kwankwaso Ya Koma Jam’iyyar ADC

Jagoran tafiyar Kwankwasiyya kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sanar da komawarsa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wani taro da ya gudana a gidansa da ke Kano, inda ya gana da magoya bayansa domin sanar da sabon matakin siyasar da ya ɗauka.

A yayin taron, tsohon gwamnan ya buƙaci magoya bayan tafiyar Kwankwasiyya da su fara yin rijistar shiga jam’iyyar ADC tare da tabbatar da sun mallaki katin zaɓe na ƙasa domin shiga harkokin siyasa a nan gaba.

Karanta Kwankwaso Zai Shiga ADC A Ranar Litinin

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan sauye-sauyen siyasa a ƙasar, musamman gabanin shirye-shiryen zaɓukan da ke tafe.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.
Exit mobile version