Hukumar zabe ta kasa ta ayyana ranar 20 ga Fabrairu, 2027 a matsayin ranar gudanar da zaben shugaban kasa na gaba.
Shugaban hukumar, Joash Amupitan, ya sanar da hakan ne yayin taron manema labarai da aka gudanar a Abuja ranar Juma’a.
Ya kuma bayyana cewa zaɓukan ‘yan majalisar tarayya za su gudana a ranar guda, yayin da zaɓukan gwamnoni da na majalisun dokokin jihohi za su gudana a ranar 6 ga Maris, 2027.
A cewarsa, hukumar ta kammala shirye-shiryen da suka dace domin tabbatar da gudanar da zabukan cikin tsari da nasara.
