An Tabbatar da Ganin Watan Azumin Ramadan a Najeriya

Fadar Mai Alfarma Sa’ad Abubakar III, Sarkin Musulmin Najeriya, ta sanar da cewa Musulman kasar za su fara azumin watan Ramadan a ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026.

Sanarwar ta tabbatar da shigar watan Ramadan mai alfarma, wanda Musulmi a fadin duniya ke gudanar da ibadar azumi  daya daga cikin ginshikan addinin Musulunci guda biyar.

A wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmi ta fitar a daren Talata, an bayyana cewa an samu sahihan rahotannin ganin watan a wurare daban daban na kasar, wanda ya sa aka ayyana ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, a matsayin ranar 1 ga watan Ramadan na bana.

Sarkin Musulmin ya buƙaci al’umma su himmatu wajen ibada tare da sanya kasar cikin addu’o’in zaman lafiya, hadin kai, da kwanciyar hankali.

A baya, hukumomin Saudiyya su ma sun sanar da ganin watan, tare da umartar Musulmi su fara azumi a ranar Laraba.

Watan Ramadan lokaci ne da Musulmi ke kara kaimi wajen ibada, kyautatawa juna, da taimaka wa mabukata domin neman lada da kusanci ga Allah. Haka kuma lokaci ne da ake ninka ladan ayyukan alheri da ibadu.

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.
Exit mobile version