Gwamnatin United States ta bukaci wasu daga cikin kananan ma’aikatan jakadancinta da ayyukansu ba su da muhimmanci su gaggauta ficewa daga wasu kasashen yankin Gabas ta Tsakiya, sakamakon karin damuwa da ake ciki kan matsalar tsaro a yankin.
Rahotanni sun bayyana cewa matakin ya shafi kasashe da dama, ciki har da Kuwait, Iraq, United Arab Emirates, Bahrain da kuma Jordan. Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar karin tashin hankali da rashin tabbas a yankin.
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta kuma shawarci ‘yan kasarta da ke zaune ko ziyara a yankin da su bi umarnin hukumomi tare da ci gaba da bibiyar kafofin watsa labarai na cikin gida domin sanin halin da ake ciki.
Tun da farko dai ofishin jakadancin Amurka da ke Kuwait ya sanar da rufe kofofinsa na wani dan lokaci, yana mai cewa matakin ya biyo bayan karin tsanantar lamuran tsaro a yankin Gabas ta Tsakiya.
