A Lebanon an Kashe Ma’aikatan Jinya 9 – WHO

World Health Organization ta bayyana cewa akalla ma’aikatan jinya tara sun mutu a hare-hare daban-daban a kudancin Lebanon, yayin da rikicin US-Israel-Iran ke kara tsananta.

Babban daraktan WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce hare-haren sun faru ne a yankuna da dama ciki har da Kfar Tibnit, Ghandouriyeh, Jezzine, Kfar Dajjal da Zoutar al-Sharqiya, inda aka kai wa jami’an lafiya hari yayin da suke kokarin ceton rayuka.

WHO ta kuma tabbatar da cewa sama da ma’aikatan lafiya 120 sun jikkata tun farkon watan Maris, yayin da adadin wadanda suka mutu a watan ya kai 51.

Rikicin ya lalata tsarin kiwon lafiya sosai, inda aka rufe asibitoci hudu da cibiyoyin lafiya 51, yayin da wasu ke aiki a rage saboda lalacewa da rashin tsaro.

Rahotanni sun nuna cewa sama da mutane 1,100 sun mutu a Lebanon kadai tun watan Maris, ciki har da yara, yayin da dubban mutane suka jikkata ko suka rasa matsuguni a yankin.

WHO ta yi kakkausar suka kan hare-haren, tana mai jaddada cewa dole ne a kare ma’aikatan lafiya da cibiyoyin lafiya bisa dokokin kasa da kasa.

 

Domin Sumun Labari, Rahotanni da dumi dumin su shiga WhatsApp: Hausa360 WhatsApp Group Twitter : Hausa360 Twitter Facebook: Hausa360 Facebook Instagram : @Hausa360 YouTube: @Hausa3600 domin gani da ido a zahiri da sauran nishadi.
Exit mobile version